Kamfanin Dillancin Labarai na Ahlul-Bayt (a.s) - ABNA – ya bayar da rahoton cewa: Kafofin yada labarai na yahudawa, sun nakalto daga wata majiya a cikin gwamnatin mamaya, sun ba da rahoton cewa yarjejeniyar da ke gab da zartuwa tsakanin Amurka da Saudiyya game da haɓaka shirin nukiliya zaman lafiya na wannan ƙasa, tana nuna "raguwar matsayin Isra'ila a gwamnatin Amurka."
Bisa ga wannan rahoto, gwamnatocin baya na Amurka sun kasance suna danganta duk wata yarjejeniya ta nukiliya da Saudiyya ga ci gaba a hanyar daidaita dangantaka da Isra'ila, yayin da wannan sharadi babu shi a yarjejeniyar yanzu. Raba batun shirin nukiliya na Saudiyya daga batun daidaita dangantaka, yana nufin rasa ɗaya daga cikin muhimman takardun matsin lamba da Tel Aviv ta dogara da su don tilasta Riyadh ta kulla dangantakar hukuma da ita.
Mihal Yaari, manazarcin Isra'ila ƙwararre kan harkokin kasashen Tekun Farisa, ta yi imanin cewa, daga mahangar wannan gwamnati, wannan yarjejeniya mataki ne da ba a taɓa yin irinsa ba; domin tana ba Saudiyya hakkin haɓaka shirin nukiliya na zaman lafiya ba tare da danganta shi da kowane ci gaba na siyasa da Isra'ila ba, lamarin da zai iya rage sha'awar Riyadh na shiga hanyar daidaita dangantaka.
Dangane da nazarin wannan shafin Larabawa, wannan yarjejeniya ta ƙunshi sassan da ke ba Saudiyya izinin, bayan nazarin hadin gwiwa da Amurka, a wasu yanayi na musamman, ta samar da wadataccen tacaccen uranium ko sake sarrafa plutonium a cikin ƙasarta, kuma wannan, baya ga shirye-shiryen sa ido, wanda ya bambanta da shirye-shiryen da aka sanya a baya ga wasu kasashe kamar UAE.
A rubutun manazarciyar shafin NASS, ƙwararrun yahudawa sun yi imanin cewa waɗannan sassan na iya ba Saudiyya ƙarfin fasaha da ake buƙata nan gaba, wanda idan wannan ƙasa ta yanke shawarar karkata zuwa shirin nukiliya na soji, za ta iya amfani da shi; ko da yake yarjejeniyar ta fayyace cewa an keɓe wannan aikin don manufofin zaman lafiya.
Dangane da wannan nazari, a gefe guda, ƙwararrun sun lura da cewa wannan yarjejeniya za ta kawo fa'idodi masu yawa ga Saudiyya; domin za ta ba wannan ƙasa damar samar da wutar lantarki ta hanyar makamashin nukiliya, wanda hakan zai ba da damar rage amfani da man fetur a cikin ƙasar, da kuma ƙara fitar da shi.
A ci gaban wannan rahoto yazo, manazarta sun yi gargadin cewa wannan yarjejeniya na iya buɗe kofa ga gasar makamai na nukiliya a yammacin Asiya, musamman a inuwar maganganun baya na Mohammed bin Salman, yarima mai jiran gado na Saudiyya, wanda a cikinsu ya yi iƙirarin cewa idan Iran ta sami makamin nukiliya, Saudiyya ma za ta yi ƙoƙarin samun shi. Haka kuma ƙwararrun sun yi imanin cewa duk wani ci gaba na irin wannan na iya tursasa wasu ƙasashe a yankin, kamar Masar da Turkiyya, su nemi shirye-shiryen nukiliya irin wannan, kuma wannan shi ne abin da zai iya ƙara sarkakiyar yanayin tsaro a Yamamcin Asiya.
Wannan matain yana zuwa ne fa a halin da Amurka ke yakar Iran akan hanata mallakar Makaman Nukiliya amma kuma yanzu gashi tana bude wani sabon shafi don bayar da dama ga kasar Saudiyya akan ta mallakin irin wannan makaman anya kuwa
Ku Bayyana Mana Ra’ayinku !!!
…………………..
Ra'ayinka